Gwamnatin Nijeriya ta musanta zargin babban jami’in Binance cewa ‘yan majalisa 3 sun nemi cin hancin $150m

-

Gwamnatin Nijeriya ta musanta zargin babban jami’in kamfanin Binance Tigran Gambaryan wanda ya shafe watanni takwas yana tsare a hannun hukumomin Nijeriya bisa zargin rashawa.
Gambaryan wanda dan kasar Amurka ne, an sake shi bayan da gwamnatin kasar ta shiga tsakani, sai dai a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X ya zargi gwamnatin Nijeriya da tsare shi ba bisa ka’ida ba.
Ya kuma yi zargin cewa wasu ‘yan majalisa uku sun nemi ya basu cin hanci na dala miliyan 150.
A martanin gwamnatin, ta hannun ministan yada labarai Mohammed Idris, ta ayyana kalaman a matsayin yunkurin yada labaran karya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara