DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tsohon gwamnan jihar Jigawa Sule Lamido ya bayyana damuwarsa kan yadda malaman addini shiga harkokin siyasa, indaj ya bayyana cewa a yanzu malamai suna da tasirin gaske a kan masu zabe da harkokin siyasa

-

 

Sule Lamido

Sule Lamido ya bayyana hakan ne a cikin wani faifan bidiyo da ke yawo, wanda ke nuna lokacin da ya kai ziyarar ta’aziyya ga Sheikh Yusuf Sambo Rigachikun a Kaduna sakamakon rasuwar babban dansa.

Tsohon ministan harkokin wajen ya koka da yadda malaman addini suke ci gaba da mamaye fagen siyasa, inda suke fitowa karara suna kamfen ga ‘yan takara tare da jagorantar mabiyansu kan wadanda za su marawa baya, ya kara da cewa duk da albarkar kasancewarsu shugabannin addini, malamai yanzu suna tallafawa masu neman mulki.

A cewar sa kamata ya yi malamai su tsaya a matsayinsu na malamai, ‘yan siyasa su tsaya a matsayinsu na ‘yan siyasa domin samun daidaito da adalci ga al’ummar da ake jagoranta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara