DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An yi garkuwa da ma’aikaci Asibitin koyarwa na jami’ar Modibbo Adama da ke Yola a jihar Adamawa da wasu mutane 3 – Rundunar ‘yan sandan jihar

-

‘Yan sanda

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta tabbatar da sace ma’aikacin asibitin koyarwa na jami’ar Modibbo Adama da ke Yola, Abubakar Sadiq Umar da wasu karin mutane uku.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Dankombo Morris, ne ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an yi garkuwa da mutanen ne a kauyen Mayokila da ke karamar hukumar Jada ta jihar.

CP Dankombo ya kara da cewa lamarin ya faru ne a lokacin da wasu gungun ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne suka mamaye yankin da sanyin safiyar ranar Litinin 17 ga watan Fabrairun 2025 inda suka fara harbe-harbe don sanya tsoro ga mutane tare da sace Umar da wasu mutane uku.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara