DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Kano, za ta yi amfani da shawarwarin kwamitin bincike kan zanga-zangar tsadar rayuwa

-

 

Abba Kabir Yusuf

Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature D/Tofa, ya fitar ranar Talata.

Gwamnan ya yi alkawarin ne a lokacin lokacin da ya karbi rahoto daga shugaban kwamitin da aka kafa da daya gudanar da bincike kan zanga zangar da aka gudanar a ranar 1 ga Agusta, 2024, bisa jagorancin mai shari’a Lawan Wada (mai ritaya), yayin taron majalisar zartarwa ta jihar Kano daya gudana a gidan gwamnati ranar Talata.

Rahoton kwamitin ya ce akalla mutane 10 ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu bakwai suka samu munanan raunuka a jihar Kano.

A cewar rahoton an kuma lalata kadarorin gwamnati da daidaikun mutane da suka haura N11bn a lokacin zanga zangar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara