DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin tarayya ta bukaci ‘yan kasuwa da su rage farashin kayan abinci

-

 

Ministan Noma da albarkatun kasa Abubakar Kyari ne ya bayyana bukatar hakan a ranar Talata, a yayin wani bikin noman alkama da aka gudanar a kauyen Dabi dake karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa.

Ministan ya bayyana takaicinsa kan yadda wasu ‘yan kasuwa suka ki sauke farashi duk da saukowar kayayyaki, yana mai bayyana hakan a matsayin rashin kishin ƙasa.

Ya ce gwamnatin tarayya tana sane da saukar farashin kayan abinci a wasu manyan kasuwanni, musamman na kayan masarufi kamar su gari, sukari, shinkafa da taliya.

Amma duk da haka wasu, masu yin burodi, da masu shaguna a cikin Unguwanni sun ki sauke farashin kayyayyakin amfanin yau da kullum, a saboda haka ya yi kira da su sauke farashi kamar yadda yake sauka a wasu kasuwanni.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna kokarin bunkasa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan 1 – Kashim Shettima

Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya ce gwamnatin kasar na kan hanyar bunkasa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan 1 cikin shekaru goma masu zuwa. Kashim...

Yan sanda sun dakile yunkurin garkuwa da direba da fasinjoji a Katsina

Jami’an rundunar ‘yan sandan Nijeriya sun dakile wani yunkurin yin garkuwa da mutane a hanyar Funtua zuwa Gusau a Katsina. Jami’an sun yi artabu da ‘yan...

Mafi Shahara