DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hisbah ta haramta ayyukan gidajen rawa a Katsina

-

 

Hukumar Hisbah ta jihar Katsina ta haramta duk wani aikin gidajen casun Nightclub dare a fadin jihar, ta ce tsarin ya yi daidai da addinin Musulunci.

Babban Kwamandan Hisbah na jihar Dakta Aminu Usman Abu-Ammar ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba.

Ya bayyana cewa dole ne masu gidajen rawa su rufe gidajensu domin dakile munanan dabi’u, da kare mutuncin al’umma, da magance matsalolin tsaro a jihar.

Hukumar ta yi gargadin cewa duk wanda ya karya doka za su fuskanci hukunci mai tsauri.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara