DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Har yanzu Nijeriya laluben shugabanni nagari take yi – Sheikh Gumi

-

Sheikh Gumi

Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Mahmoud Gumi, ya ce har yanzu Nijeriya na neman shugabannin da za su ciyar da kasar gaba.

A cewarsa, irin wadannan shugabanni su ne wadanda ke fifita jin dadin ‘yan kasa fiye da tara dukiya.

Malamin ya bayyana hakan ne a yayin bikin karramawa da kungiyar tsofaffin daliban makarantar Sultan Bello (SUBOPA) ta shirya domin karrama mambobinsu guda biyu Manjo Janar Abdulmalik Jibrin (Rtd) da Birgediya Janar Abdulkadir Gumi (Rtd) wanda ya samu mukamin gwamnati kwanan nan. 

Gumi ya bayyana Manjo Janar Jibrin a matsayin hafsan soja mai himma, da’a, da kuma kwazo a lokacin aikin sa, inda ya ce Nijeriya na bukatar mutane irinsa a matsayin shugabanci saboda jajircewa da kishin kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara