DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mune ‘ya’yan jam’iyyar NNPP ta asali, Alhassan Rurum yayi fatali da dakatarwar da jam’iyyar NNPP ta yi masu a Kano

-

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Rano, Kibiya, da Bunkure a majalisar wakilan Nijeriya, Hon. Kabiru Alhassan Rurum, ya yi watsi da dakatarwar da aka yi masa daga jam’iyyar NNPP a Jihar Kano.

Da yake mayar da martani kan sanarwar dakatarwar da shugaban jam’iyyar NNPP na jihar Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa ya fitar, Kabiru Alhassan Rurum ya ce shi da takwarorinsa da aka dakatar ba su taba bin bangaren da suka sauya tambarin jam’iyyar ba, yana mai jaddada cewa suna cikin jam’iyyar ta asali.

A baya dai Alhassan Rurum da Aliyu Sani Madakin Gini sun fito fili sun ware kansu daga tafiyar Kwankwasiyya tare da jaddada kansu a cikin Jam’iyyar NNPP mai alamar kayan marmari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara