DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da wasu dalibai mata 4 a jihar Benue

-

 

Google search engine

Rundunar ‘yan sandan jihar Benue ta tabbatar da sace dalibai mata 4 na jami’ar aikin gona ta gwamnatin tarayya da ke Makurdi.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Benue, CSP Sewuese Anene, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa ta wayar tarho da gidan talabijin na Channels, inda ya ce an fara gudanar da bincike tare da nemo inda suke.

Wasu majiyoyi a kusa da jami’ar sun ce wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da daliban ne a harabar jami’ar da misalin karfe 8:30 na dare, lamarin da ya haifar da firgici ga daliban.

Yace daliban da aka yi garkuwa da su sun hada da, Emmanuella Oraka, Fola, Susan da kuma Ella.

A halin da ake ciki dai labarin sace daliban ya haifar da zanga-zanga daga daliban da suka zagaye makarantar inda suka bukaci mahukuntan makarantar su dauki matakin gaggawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna biyan ‘yan bindiga Naira miliyan 7 don zama a gidajenmu ko noma gonakinmu

Wasu al’ummomi a karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja sun bayyana cewa suna biyan haraji ga ‘yan bindiga domin su samu damar zama a garuruwansu...

Abin takaici ne a ce tawagar Super Eagles na bin bashi – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023 Peter Obi, ya bayyana takaici kan rahotannin da ke nuna cewa tawagar wasan...

Mafi Shahara