DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da wasu dalibai mata 4 a jihar Benue

-

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Benue ta tabbatar da sace dalibai mata 4 na jami’ar aikin gona ta gwamnatin tarayya da ke Makurdi.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Benue, CSP Sewuese Anene, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa ta wayar tarho da gidan talabijin na Channels, inda ya ce an fara gudanar da bincike tare da nemo inda suke.

Wasu majiyoyi a kusa da jami’ar sun ce wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da daliban ne a harabar jami’ar da misalin karfe 8:30 na dare, lamarin da ya haifar da firgici ga daliban.

Yace daliban da aka yi garkuwa da su sun hada da, Emmanuella Oraka, Fola, Susan da kuma Ella.

A halin da ake ciki dai labarin sace daliban ya haifar da zanga-zanga daga daliban da suka zagaye makarantar inda suka bukaci mahukuntan makarantar su dauki matakin gaggawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara