DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Bauchi ta ba da hutun makarantu saboda gabatowar watan Ramadan

-

 

Bala Muhammad Abdukadir

Gwamnatin jihar Bauchi, ta hannun ma’aikatar ilimi ta sanar da rufe dukkanin makarantun jihar a shirye shiryen fara azumin watan Ramadan na 2025 na tsawon makonni biyar.

Hakan na kunshe a cikin wata sanarwar da ma’aikatar ilimi ta jihar ta fitar.

Da yake zantawa da Kamfanin dillancin labaran Nijeriya (NAN), jami’in yada labarai na ma’aikatar ilimin Jalaludeen Maina ya ce dama tun kafin wannan lokaci aka sanya yadda tsarin hutun zai kasance a cikin kalanda.

Ya bayyana cewa fara hutun zai fara ne daga ranar 1 ga Maris har zuwa 5 ga Afrilu wanda ya kama sati biyar kenan.

Maina ya ce hutun ya shafi dukkanin makarantun da suka hada da na gwamnati da masu zaman kansu na firamare da na sakandare da kuma manyan makarantun jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara