HomeUncategorizedJam'iyyar NNPP a Nijeriya ta bukaci El-Rufai ya nemi afuwarta bisa zargin...

Jam’iyyar NNPP a Nijeriya ta bukaci El-Rufai ya nemi afuwarta bisa zargin da ya yi mata

-

Tsohon gwamnan jihar Kaduna 

Jam’iyyar NNPP ta kasa ta yi Allah-wadai bisa zargin da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i, ya yi wa jam’iyyar cewa gwamnatin tarayya ce ta dauki nauyinta dangane da korar tsohon dan takararta na shugaban kasa, Rabiu Kwankwaso da kuma dakatar da gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf.

Sakataren jam’iyyar na kasa, Oginni Olaposi, ne ya yi wannan Allah-Wadai ta cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba.

Ta cikin sanarwar NNPP ta zargi El-Rufai, da kokarin kawar da hankalin mutane daga ainihin abubuwan da ke faruwa yanzu haka.

Tsohon gwamnan na Kaduna wanda a baya-bayan nan ya sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa SDP, ya yi zargin cewa gwamnatin tarayya ce ke rura wutar rikicin jam’iyya mai mulki da kuma na jam’iyyun adawar kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img