Jami’an tsaro sun dakile harin ‘yan bindiga a Katsina, tare da ajalin mutum daya

-

‘Yan sanda

Jami’an tsaro sun dakile wani hari da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai a karamar hukumar Danmusa da ke jihar Katsina.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, DSP Abubakar Sadiq, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

Ya ce aikin da aka yi a ranar Asabar din da ta gabata ya kasance tare da hadin gwiwar ma’aikatar ayyuka ta jihar, da kuma ‘yan kungiyar sa kai ta jihar Katsina.

 A cewarsa, ‘yan bindigar sun yi yunkurin kai hari kauyen Dan Takuri na karamar hukumar Danmusa da ke jihar.

 A ranar 15 ga Maris, 2025, bayanan sirri da aka samu daga jami’an tsaro na farin kaya a Danmusa, ‘yan bindigar masu tarin yawa sun hau tsaunin Maijele da ke karamar hukumar Danmusa a yunkurin kai hari kauyen Dan Takuri.

Bayan samun labarin, ba tare da bata lokaci ba, tawagar hadin guiwar jami’an ‘yan sanda da ‘yan karkashin jagorancin DPO Danmusa suka afkawa tsaunin da ake zargin ‘yan fashin ne suke taruwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara