HomeUncategorizedKungiyar SERAP ta maka Akpabio a kotu kan dakatar da Natasha Akpoti...

Kungiyar SERAP ta maka Akpabio a kotu kan dakatar da Natasha Akpoti Uduaghan

-

Godswill Akpabio

Kungiyar SERAP mai fafutikar yaki da cin hanci da rashawa a Nijeriya ta yi karar shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, kan kin sauya matakin dakatarwar da aka yi wa Sanata Natasha Akpoti ba bisa ka’ida ba,wanda ta ce hakan take ‘yancinta ne na fadin albarkacin bakinta.

A kwanakin baya ne majalisar dattawa ta dakatar da Natasha Akpoti-Uduaghan na tsawon watanni shida, bayan da aka ce ta ‘yi magana ba tare da izini ba’ kuma ta ‘ki amincewa da sabuwar kujerar da aka ware mata a zauren majalisar.

A cikin karar mai lamba FHC/ABJ/CS/498/2025 da aka shigar a ranar Juma’ar da ta gabata a babbar kotun tarayya da ke Abuja, SERAP na neman da a tilasta soke dakatarwar da aka yi wa Natasha Akpoti-Uduaghan ba bisa ka’ida ba, a maido da ita, tare da dawo mata da dukkan hakkokinta.

SERAP na neman Majalisar Dattawa da ta dakatar da daukar duk wani matakin ladabtarwa a kan Natasha Akpoti-Uduaghan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img