DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Atiku da Peter Obi, sun bukaci majalisun dokoki da su yi watsi da dokar ta-baci da Tinubu ya kakaba a jihar Rivers

-

Atiku Abubakar/Peter Obi

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, tare da na jam’iyyar Labour, Peter Obi, da sauran jiga-jigan ‘yan adawa sun yi kira ga majalisun dokokin kasar da su yi watsi da kakaba dokar ta baci a jihar Rivers da shugaba Bola Tinubu ya yi.

Atiku, wanda ya yi magana a madadin ‘yan adawar a wani taron manema labarai a Abuja ranar Alhamis, ya zargi Tinubu da nuna son kai da kuma amfani da sashe na 305 da bai dace ba game da sanya dokar ta baci.

Ya yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta soke wannan dakatarwar da yayi da ta sabawa kundin tsarin mulkin kasar, ya maido da zababben gwamna da mataimakiyar sa, da majalisar dokokin jihar Rivers.

Idan dai za a iya tunawa, Jihar Rivers ta kwashe kusan shekaru biyu tana fama da rikice-rikicen siyasance, yayin da tsohon Gwamna Nyesom Wike da magajinsa, Siminayi Fubara ke fafatawa da juna, lamarin da ya janyo cece kuce a jihar.

A dalilin haka ne shugaban ya kakaba dokar ta baci a jihar a ranar Talata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara