DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotun koli ta tabbatar da Samuel Anyanwu, a matsayin sakataren PDP na Kasa

-

Kotun koli a Nijeriya ta tabbatar da Samuel Anyanwu, kuma na hannun daman ministan birnin tarayya Abuja a matsayin sakataren jam’iyyar PDP na kasa.

Samuel Anyanwu da Sunday Ude Okoye dai sun yi takun-saka tsakaninsu, lamarin da ya janyo rarrabuwar kawuna a tsakanin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

Sai dai Ude Okoye ya samu goyon baya daga bangarori daban-daban na jam’iyyar wadanda suka dogara da hukuncin da wata kotun daukaka kara da ke zamanta a Enugu ta yanke.

Kotun daukaka karar ta tabbatar da tsige Anyanwu da wata babbar kotun tarayya da ke Enugu ta yi.

Sai dai a wani hukunci da aka yanke a ranar Juma’a, kotun mai alkalai biyar, yayin zartar da hukuncin ta ce al’amuran da suka shafi shugabanci a jam’iyyar siyasa al’amari ne na cikin gida, kuma bai kamata ya zama na kotu ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara