Kwankwaso ya caccaki Tinubu kan dakatar da gwamnan Rivers

-

Rabi’u Musa Kwankwaso
Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP kuma jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi kakkausar suka ga matakin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya dauka na kakaba dokar ta baci a jihar Rivers, inda ya ce hakan hadarine ga dimokuradiyyar Nijeriya. 
A wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, Kwankwaso ya bayyana matukar damuwarsa kan dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara, da mataimakinsa, da kuma daukacin ‘yan majalisar dokokin jihar da aka zaba, inda ya bayyana matakin a matsayin wuce gona da iri.
Sanata ya yi gargadin a guji maimaita kura-kuran da aka yi a baya, inda ‘yan majalisa suka shagaltu da rigingimun cikin gida maimakon kare tsarin dimokuradiyya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara