DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Zargin nadin mukamai da ake yi wa shugaban NAHCON yarfe ne – Kungiyar Matasan Arewa ta Progressive Northern Youth

-

Farfesa Abdullahi Sale Usman

Kungiyar Progressive Northern Youth PNY, ta musanta zargin nuna son kai da kuma rashin adalci da ake yi wa shugaban hukumar alhazai ta Nijeriya NAHCON, Farfesa Abdullahi Sale Usman.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, Ko’odinetan kungiyar Dr, Muktar Suleiman,ya bayyana zargin a matsayin mara tushe, yana mai cewa wannan aikin ‘yan zagon kasa ne, wadanda suke son su kawar da hankalin hukumar daga aikinta.

A cewarsa, wasu mutanen da ba su ji dadin nasarorin da hukumar ta samu a karkashin jagorancin Farfesa Usman, suna aiki tukuru don ganin sun tozarta sunansa da na gwamnatin Tinubu.

Suleiman ya kara da cewa, kwararan hujjoji sun tabbatar da cewa babu manyan jami’an hukumar ko shugabanninta da ke yin katsalandan ga ka’idojin da aka gindaya da ke jagorantar ayyukan hukumar.

Ya bukaci ‘yan Nijeriya masu kishin kasa da su rika samun sahihin bayanai daga hukumar kafin su je ga manema labarai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara