Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta sanar da zaman makoki na kwana uku bayan ‘yan ta’adda sun yi ajalin mutum 44 a masallaci

-

Abdoulrahmane Tiani

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta sanar da zaman makoki na kwana uku a kasar  bayan ajalin wasu mutane 44 a kudu maso yammacin ƙasar a wani hari da ake zargin “yan ta’adda” da ke da alaƙa da ƙungiyar ta’addanci ta Daesh suka kai.

Ma’aikatar harkokin cikin gida ta ƙasar Nijar ce ta sanar da hakan a wata sanarwa da ta fitar a gidan talabijin na ƙasar a ranar Juma’a.

Ma’aikatar ta ce ‘yan ta’addan sun yi ajalin mutanen ne a lokacin da suka afka cikin wani masallaci a ƙauyen Fombita da ke Kokorou inda suka far wa masallata.

Ma’aikatar ta yi Allah-wadai da harin tare da shan alwashin ƙara matsa ƙaimi domin yaƙi da ta’addanci a yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara