HomeUncategorizedKotu ta hana INEC karbar takardar koke da nufin fara yi wa...

Kotu ta hana INEC karbar takardar koke da nufin fara yi wa Sanata Natasha Akpoti kiranye

-

Wata babbar kotun tarayya da ke Lokoja a ranar Juma’a ta hana hukumar zabe ta kasa INEC karbar takardar korafe-korafe da nufin fara shirin yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan kiranye.

Mai shari’a Isa Dashen, ne  ya ba da umarnin  bayan karar da aka shigar gabansa.

Masu shigar da kara, Anebe Jacob Ogirma, John Adebosi, Musa Adeiza,  Ahmed Usman, da kuma Maleek Yahaya, sun shigar da karar ne ta hannun lauyoyinsu suna neman a hana INEC karbar  kudirin kiranyen na  matakin da ake shirin dauka kan Sanata Akpoti-Uduaghan, Sanata mai wakiltar mazabar Kogi ta tsakiya.

Sun nemi kotun da ta umurci INEC da kada ta karbi koke daga wasu da ake zargi da nufin fara shirin yi wa Sanatan kiranyen.

Mai shari’a Isa Dashen ya amince da bukatar kuma ya bayar da umarnin a mika umarnin ga wanda ake kara wato INEC,tare da sanya ranar 6 ga Mayu don ci gaba da sauraron karar kamar yadda kamfanin dillancin labaran Nijeriya NAN ya ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img