Iran ta samu tikitin shiga gasar cin kofin Duniya ta 2026

-

Tutar Kasar Iran 

Bayan tashi wasa chanjaras biyu da biyu tsakaninta da Uzbekistan a filin wasa na Azadi da ke Tehran a Talatar nan, Iran ta samu tikitin shiga gasar cin kofin Duniya ta 2026.

Dan wasan Iran da ke taka leda a Intermilan, Mehdi Taremi, ne ya zura kwallaye biyu bayan dawowa daga hutun rabin lokaci a fafatawar, lamarin da ya baiwa tawagar ta Iran damar shiga gasar karo na hudu a jere, jimulla karo na bakwai a tarihi. 

Tawagar Uzbekistan ce ta fara jan ragamar wasan bayan da Dan wasa Khojimat Erkinov ya zura kwallo a minti na 16, sai dai Taremi ya sauya lamarin a minti na 52, yanzu haka dai Iran ita ce ta farko da maki 20 a rukunin A na gasar cancantar shiga gasar cin kofin Duniya a yankin Asia.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara