DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An samu mutane 886 da ake zargin sun kamu da cutar kwalara cikin makonni biyar a Nijeriya – NCDC

-

Hukumar hana yaduwar cututtuka a Nijeriya NCDC ta bayyana cewa an samu rahoton mutane 886 aka yi zargin sun kamu da cutar kwalara ta kuma halaka mutane 14 a cikin makonni biyar na farko na farkon shekara, tsakanin 27 ga Janairu zuwa 2 ga Fabrairun 2025.

Hukumar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, inda ta kara da cewa an samu bullar cutar a jihohi 22 na kasar baki daya.

Rahoton ya nuna karuwar kashi 75 cikin 100 na wadanda suka kamu da cutar da kashi 250 na mace-mace idan aka kwatanta da na shekarar 2024.

A cewar NCDC, jihar Bayelsa ce ke da kashi 78 cikin 100 na masu dauke da cutar da mutane 695 da ake zargin sun kamu da ita. 

Sauran jihohin da cutar ta bulla sun hada da Rivers 54, Niger 33, da Abia da ke da 32.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna kokarin bunkasa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan 1 – Kashim Shettima

Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya ce gwamnatin kasar na kan hanyar bunkasa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan 1 cikin shekaru goma masu zuwa. Kashim...

Yan sanda sun dakile yunkurin garkuwa da direba da fasinjoji a Katsina

Jami’an rundunar ‘yan sandan Nijeriya sun dakile wani yunkurin yin garkuwa da mutane a hanyar Funtua zuwa Gusau a Katsina. Jami’an sun yi artabu da ‘yan...

Mafi Shahara