DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojin Nijeriya 171 za su je kasar Sudan domin aikin wanzar da zaman lafiya a kasar

-

Sojoji

Rundunar sojin Nijeriya ta sanar da tura dakarunta 171 zuwa yankin Abyei da ke kan iyakar Sudan ta Kudu domin aikin wanzar da zaman lafiya.

Babban hafsan Sojojin Nijeriya, Manjo-Janar Boniface Sinjen, ya bayyana hakan ne a Jaji Military Cantonment dake Kaduna, lokacin da yake jawabi ne ga sojojin da suka yaye na tawagar Nijeriya ta 3, da za a tura zuwa Abyei karkashin rundunar tsaro ta Majalisar Dinkin Duniya (UNISFA).

Ya jaddada muhimmancin aikin, inda ya bayyana cewa, ayyukan wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya ba aikin soja ba ne kawai, aiki ne na tabbatar da zaman lafiya, diflomasiyya, da hidima ga al’umma.

Ya kuma bayyana cewa Nijeriya na da tarihi mai kyau a ayyukan wanzar da zaman lafiya, inda dakarunta ke taka rawar gani wajen maido da zaman lafiya a yankunan da ake fama da rikici a fadin Afrika da ma duniya baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara