HomeUncategorizedAtiku Abubakar ya musanta karbar tallafin kudin kamfe daga Gwamna Sanwo Olu...

Atiku Abubakar ya musanta karbar tallafin kudin kamfe daga Gwamna Sanwo Olu na jihar Lagos a lokacin zaben 2023

-

Atiku Abubakar

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar musanta ikirarin da ake na cewa gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu ya bashi tallafin kudi na yakin neman zabe a zaben shugaban kasa da ya gabata.

A wata sanarwa da mai magana da yawun sa Paul Ibe ya fitar, ofishin yada labarai na Atiku ya karyata rahotannin da ke nuni da cewa Sanwo-Olu, ta hannun Ms. Aisha Achimugu, ya bai wa tsohon mataimakin shugaban kasa kudi da ake zargin mallakar jihar Legas ne, abinda ya kira makircin ‘yan siyasa da suka kulla.

A farkon makon da ya gabata ne jaridar PREMIUM TIMES ta ruwaito cewa ana binciken Ms Achimugu kan zargin karkatar da kudade da dama.

Hukumar EFCC mai yaki da cin hani da rashawa a Nijeriya na ci gaba da binciken matar da ake zargi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img