DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Masu garkuwa da mutane sun yi awon gaba da mutam shida a Kogi

-

Usman Ododo

 Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun yi garkuwa da wasu mutane shida na al’ummar Ayetoro-Kiri da ke karamar hukumar Kaba-Bunu ta jihar Kogi.

Jaridar The Guardian ta bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Alhamis, inda ‘yan bindigar da ke kan babura suka mamaye yankin.

‘Yan bindigar sun fara kai hari ne a wani shagon sayar da wayoyin tare da kwashe wayoyin hannu sama da 50 inda suka rika harbin bindigogi kai tsaye.

Shaidun gani da ido sun ce ‘yan bindigar sun kama al’ummar garin domin karbar kudin fansa, lamarin da ya haifar da tashin hankali ga al’ummar yankin,bayanai ya sun tabbatar da cewa masu garkuwa da mutanen ba su tuntubi iyalan wadanda abin ya shafa ba har ya zuwa lokacin hada wannan lokacin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara