DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan jihar Jigawa Umar Namadi ya bayyana shirin gwamnatinsa na yi wa makiyaya rijista a jihar sakamakon karuwar kwararar makiyaya daga jamhuriyar Nijar zuwa Jigawa

-

Malam Umar Namadi

Gwamnan jihar Jigawa Umar Namadi ya bayyana shirin gwamnatinsa na yi wa makiyaya rijista a jihar sakamakon karuwar kwararar makiyaya daga jamhuriyar Nijar zuwa Jigawa 

Gwamna Namadi ya bayyana damuwar sa kan yadda ake samun karuwar mace-mace da raunata mutane da rakuma wadanda suka fito daga jamhuriyar Nijar, yayin da suke tsallaka manyan tituna a jihar.

Jihar Jigawa,na daya daga cikin jihohin Arewa maso Yammacin kasar da ke makwabtaka da jamhuriyar Nijar, kasar da ta shahara wajen kiwon rakuma, da a yanzu haka ke samun  yawaitar hadurran da ke da alaka da rakuma akan hanyoyin ta.

An bayyana cewa, rakuma wadanda suka saba kiwo da dare, suna tsallaka kan iyaka daga kasar Nijar zuwa cikin Nijeriya, suna yawo a sassan jihar Jigawa lamarin da ke haddasa hadurra da dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara