HomeUncategorizedKungiyar Sanatocin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan gillar matafiya-mafarauta a...

Kungiyar Sanatocin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan gillar matafiya-mafarauta a Edo

-

Majalisar Dattawa

Kungiyar Sanatocin Arewa ta yi Allah-wadai da kisan mafarauta-matafiya da aka yi a Uromi, karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas a jihar Edo.

 A wata sanarwa da shugaban kungiyar Sanatocin Arewa, Abdulaziz Yar’adua ya fitar a Abuja, ‘yan majalisar sun bayyana lamarin a matsayin abu  ‘mai matukar tayar da hankali da bakin ciki.

A cewar sa  mafarautan  da suka tafi daga yankin Arewacin Nijeriya, an yi musu  kisan gilla na wulakanci, na ba gaira ba dalili  don haka sun yi Allah wadai da wannan danyen aikin, sun kuma yi kira ga gwamnatin Jihar Edo da ta dauki matakin gaggawa domin zakulo  batagarin  da suka aikata wannan kisan  tare da hukunta su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img