DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An gudanar da Jana’izar mutane 16 da aka yi ajalin su a Edo

-

Bola Ahmed Tinubu

 

An binne gawarwakin mutane 16 da suka rasa rayukansu a mummunan harin da aka kai musu a Jihar Edo.

Al’ummar Hausawa  da abokan arziki,  ne suka  taru domin  alhini da yin addu’o’i ga marigayan bayan yi musu Jana’iza tare da binne gawarwaki 16 a jihar ta Edo 

Yayin da gwamnati ta ce tana bincike a kan kisan, kungiyoyin kare hakkin bil’adama da na Addinai da sauran al’umma na ci gaba da yin Allah wadai da harin, tare da kiran lallai a hukunta wadan da suka yi aika aikar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara