DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fitacciyar ‘yar jarida kuma mai fafitika a shafukan sadarwa Samira Sabo, ta yi fatan ganin an saki hambararren shugaban Nijar Mohamed Bazoum

-

‘Yar jarida a Nijar wacce ta yi fice a baya wajen sukar gwamnatin jamhuriyar ta 7 ta tsohon shugaban kasa Issoufou Mahamadou da magajinsa Mohamed Bazoum ta ziyarci gidan shugaba Issoufou Mahamadou domin taya shi murnar sakin abokan gwagwarmayar siyasarsa. 
Samira a cikin sakon da ta wallafa a shafinta na Facebook, ta ce watanni biyu da suka gabata ta samu ganawa da tsohon shugaban kasar inda ta bukaci da ya shiga cikin lamarin siyasar kasar domin samar da mafita akan dambarwar siyasar da ake ke ciki.
‘Yar jaridar ta ce a nata ra’ayi, mataki na gaba ya kasance na sakin hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum tare da tattaunawa da magoya bayansa har ma wadanda suke hijira a ketare.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara