DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotun sauraren kararrakin zabe ta yi watsi da ƙarar jam’iyyar AA da ke kalubalantar zaben Monday Okpebholo na APC a matsayin gwamnan jihar Edo

-

Kotun sauraren kararrakin zaben gwamnan jihar Edo da ke Abuja ta yi watsi da karar da jam’iyyar Action Alliance da Dan takararta Adekunle Omoaje suka shigar kan zaben gwamna Monday Okpebholo da jam’iyyar APC da kuma hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa. 
A hukuncin da ta yanke a ranar Laraba, kotun mai alkalai uku ta yi fatali da karar, saboda rashin gamsassun hujjoji. 
Jam’iyyar AA da Omoaje sun kalubalanci nasarar Okpebholo ya samu a zaben gwamna da aka yi a ranar 21 ga Satumba, 2024, bisa zargin rashin bin dokar zabe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara