DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar ‘yan sandan Kano za ta yi bincike kan zargin take dokar hana yin hawan sallah a jihar

-

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kafa kwamitin da zai bincike kan hatsaniyar da ta faru yayin da Sarki Muhammad Sanusi ke wucewa bayan gabatar da Sallar Idi, da kuma duk wani zargin take dokar hana yin hawan sallah da aka kafa a jihar.
Sanarwar da kakakin rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar tace, an ɗora wa kwamitin mai mutum takwas alhakin gano musabbabin faruwar tashin hankalin da ya yi sanadin rayuwar wani ɗan vigilante ɗaya da jikkata wani mutum ɗaya.
Sanarwar ta kara da cewa, Kwamishinan ‘yan sandan Kano ya umurci kwamitin ya bincike zargin taka dokar hana hawan sallah da aka yi kuma tuni aka gayyaci Shamakin Kano, Alhaji Wada Isyaku domin amsa tambayoyi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara