Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima zai wakilci shugaba Tinubu a kasar Senegal wajen bikin cika shekara 65 da samun ‘yancin kan kasar

-

Kashim Shettima

 Mataimakin shugaban kasar Shettima ya bar Abuja ne zuwa Dakar domin ya wakilci shugaba Tinubu a wajen bikin cikar Senegal shekaru 65 da samun ‘yancin kai.

Kasar Senegal na bikin ranar samun ‘yancin kai a ranar 4 ga watan Afrilun kowace shekara, inda ake bikin ‘yancin kai daga turawan mulkin mallaka na Faransa a shekara ta 1960.

Ranar dai ta kasance cikin alfahari da al’ummar kasar, tare da shagulgula, da yin fareti da wasanni na al’adun kasar.

Halartar mataimakin shugaban kasa a taron na shekara-shekara, don girmama goron gayyatar da shugaban kasar Senegal, Bassirou Diomaye Faye ya yi wa shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya biyo bayan kyakkyawar alakar da ke tsakanin Nijeriya da Senegal.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara