Kungiyar ECOWAS za ta yi zama kan harajin da kasashen Nijar, Mali da Burkina Faso suka ƙaƙaba wa ƙasashen kungiyar

-

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS za ta gudanar da taro a cikin watan Afrilun da muke domin tattaunawa kan harajin kashi 0.5 cikin 100 na shigo da kaya da kasashen yankin Sahel suka ƙaƙaba wa ƙasashen kungiyar ECOWAS a baya-bayan.
Shugaban sashen yaɗa labarai na Hukumar ECOWAS Joel Ahofodji, ya tabbatar da cewa majalisar kungiyar za ta yi taro a ranar 22 ga Afrilu don tattaunawa kan lamarin da sauran batutuwan da suka shafi kasashen, a cewar jaridar Dailytrust.
Da aka tambaye shi ko ECOWAS za ta dauki wani mataki na ramuwa dangane da harajin kashi 0.5 da AES suka sanya, Joel Ahofodji ya bayyana cewa, kungiyar za ta tattauna kan matakin da zata dauka a lokacin taron.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara