Babban Hafsan Sojin Kasa ya kai ziyara Plateau bayan harin da ya halaka mutane da dama

-

 

Babban hafsan sojin kasa na Najeriya, Laftanar Janar Oluyemi Oluyede, ya kai ziyara zuwa karamar hukumar Bokkos a jihar Plateau, sakamakon harin ’yan bindiga da ya yi sanadin mutuwar sama da mutane 60.  

Janar Oluyede ya jagoranci tawagar manyan hafsoshin soji domin duba irin barnar da aka yi, ciki har da asarar rayuka da lalata dukiyoyin al’umma.  

Ana sa ran zai gana da shugabannin al’umma da na Fulani a yankin, tare da masu ruwa da tsaki, domin samun fahimtar juna da nemo hanyoyin magance rikice-rikice a yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara