Kasashen AES sun janye Jakadunsu daga Aljeriya bayan zargin kakkabo jirgin Mali

-

Mali/Nijar/Burikina Faso

Kasashen kungiyar AES sun janye jakadunsu daga kasar Aljeriya, bayan zargin da kasar Mali ta yi cewa Aljeriya ta harbo mata jirgin yaki marar matuki a ranar 31 ga Maris zuwa safiyar 1 ga Afrilu.  

A cewar sanarwar da gwamnatin Mali ta fitar, an harbo jirgin mai kirar TZ-98D a yankin Tin-Zaouatène da ke jihar Kidal, kusa da iyakar Aljeriya.

Gwamnatin Mali ta zargi Aljeriya da keta huruminta da kuma amfani da makami mai linzami wajen kakkabo jirgin. 

Sai dai daga bisani, Aljeriya ta bayyana a kafafen yada labaranta cewa ta kakkabo wani jirgi da ya shige sararinta da kusan kilomita biyu, zargin da Mali ta musanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara