Rashin tsaro da tashe-tashen hankula sun ragu da kashi 90% a Nijeriya – Ribadu

-

Nuhu Ribadu

Mai bai awa shugaban Nijeriya shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu ya bayyana cewa Nijeriya ta samu ci gaba sama da kashi 90 cikin 100 akan rashin tsaro a gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

Ribadu ya bayyana haka ne a garin Jos na jihar Filato a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan wata ganawa da kwamandan rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo Janar Folusho Oyinlola a ofishinsa, biyo bayan harin da ‘yan bindiga suka kai kan al’ummar Bokkos wanda ya yi sanadin mutuwar mazauna garin.

A cewarsa, gwamnatin shugaba Tinubu ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a kasar nan.

Ya ce cikin shekaru 2 da suka wuce, an samu ragin yawan mace-mace da  tashin hankali da kusan kashi 90 cikin 100 a kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara