Sudan ta kauracewa taron Birtaniya kan rikicin kasarta

-

 

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sudan ta bayyana rashin amincewarta da kuma kauracewa wani babban taro da Birtaniya ke shirin gudanarwa a tsakiyar watan Afrilu a birnin London, wanda zai tattauna rikicin Sudan.  

A cikin wata wasika da ya aikewa Sakataren Harkokin Wajen Birtaniya, David Lammy, Ministan Harkokin Wajen Sudan, Ali Yousif, ya soki matakin Birtaniya na gayyatar wasu kasashe kamar UAE, Chadi da Kenya, wadanda Sudan ke zargi da marawa dakarun Rapid Support Forces (RSF) baya.  

Taron dai na gudana ne tare da hadin gwiwar Tarayyar Turai (EU), Faransa, da Jamus, da nufin lalubo mafita kan rikicin da ya dabaibaye kasar Sudan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara