DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kudurin kayyade shekarun ’yan takarar Shugaban kasa da Gwamna ya tsallake karatu na biyu

-

Majalisar wakilai

Majalisar Wakilai ta amince da kudurin da ke neman kayyade shekarun masu neman kujerar shugaban kasa da na gwamna zuwa karancin shekaru 60, yayin da kudirin ya tsallake karatu na biyu a zauren majalisar.

Kudurin wanda dan majalisa Ikeagwuonu Ugochinyere, mai wakiltar mazabar Ideato ta Arewa daga jihar Imo, ya gabatar, yana neman a gyara sashe na 131 da na 179 na kundin tsarin mulkin Nijeriya.

A cewar Ugochinyere, ya kamata a sabunta tsarin ne domin bai wa sabbin jini damar shiga tafiyar siyasa, tare da tabbatar da cewa wadanda ke rike da manyan mukamai na kasa suna da kuzari da sabbin dabaru.

Yanzu haka, kudurin na jiran ci gaba da tattaunawa da nazari a matakai na gaba kafin ya kai ga zama doka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara