DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Natasha ta maka sanata Nwebonyi a gaban kotu kan zargin bata mata suna

-

 

Natasha Akpoti

Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta maka Sanata Onyekachi Nwebonyi a kotu tana neman diyya naira biliyan biyar bisa zargin bata suna da zarge-zargen da ke barazana ga martabarta.

Kotu ta karɓi karar ne bayan Sanata Nwebonyi ya yi wasu kalamai a taron manema labarai da Natasha ke zargin an taba kimarta a zarge- zarge marasa tushe, waɗanda suka shafi mutuncinta da rayuwarta ta siyasa.

Lauyan Sanata Natasha Michael Jonathan Numa, da ya shigar da karar, mai lamba Suit No: W/1359:25 a babbar kotun birnin tarayya Abuja ya ce kalaman sun janyo mata tozarta a idon jama’a kuma suna iya gurgunta aikinta a majalisa.

Sanata Nwebonyi bai mayar da martani ba tukuna, amma ana sa ran kotu za ta fara sauraron shari’ar nan ba da jimawa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara