‘Yan kwamitin gudanarwar hukumar NAHCON sun kai karar Farfesa Pakistan ga Shettima

-

Wasu daga cikin ‘yan kwamitin gudanarwa na hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya sun kai karar shugaban hukumar ga ofishin mataimakin shugaban kasa. 

Mambobin kwamitin na zargin shugabban NAHCON Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan da watsi da su a shirye-shiryen aikin hajjin 2025. 

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa mambobin kwamitin gudanarwa na NAHCON da suka rattaba hannu a takardar korafin sun hada da Professor Muhammad Umaru Ndagi da Alhaji Abba K. Jato da Shaykh Muhammad Bn Uthman da Hajiya Aishat Obi da Hajiya Zainab Musa da kuma  Dr Tajudeen Abefe Oladejo, sai  Professor Adedimeji Mahfouz Adebola tare da Professor Musa Inuwa Fodio 

Mambobin sun yi zargin cewa shugabancin hukumar NAHCON bai tuntube su ba a wajen tsayar da farashin kudin kujerar hajjin bana da kuma wajen zabar kamfanonin da za su yi alhazai hidima a hajjin na bana. 

Kawo yanzu hukumar ta NAHCON ba ta ce komai ba a kan wannan zargin, sai dai a wata hira da DCL Hausa a kwanakin baya, shugaban hukumar Farfesa Pakistan ya ce babu wani abu da suke yi da ya saba wa doka, yana mai jaddada cewa shugabancinsa walwalar alhazai ya sanya a gaba.



LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara