DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ku daina biyan kudin fansa ga masu garkuwa da mutane – Kiran Malam Nuhu Ribadu ga ‘yan Nijeriya

-

Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya bukaci ’yan Najeriya da su daina biyan kudin fansa ga masu garkuwa da mutane, yana mai cewa hakan na kara karfafa ayyukan ’yan ta’adda a fadin kasar.
Ribadu ya bayyana hakan ne a yayin da yake karbar wasu mutane 60 da aka ceto daga hannun masu garkuwa da mutane a karamar hukumar Zangon Kataf, Jihar Kaduna. Wadanda aka sace din an kubutar da su ne bayan wani samame da jami’an tsaro suka kai sansanin ’yan ta’addan a yankin.
A cewarsa, biyan kudin fansa na taimaka wa masu aikata laifin wajen ci gaba da wannan mummunar sana’a, yana mai kira ga al’umma da su hada kai da hukumomin tsaro domin kawar da matsalar gaba daya.
Ya kuma yaba da kokarin da dakarun soji da sauran jami’an tsaro ke yi wajen yaki da ayyukan garkuwa da mutane da sauran kalubalen tsaro a fadin kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara