DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna Allah-wadai da fara yakin neman zabe na 2027 da ‘yan siyasa ke yi, ku mayar da mayar da hankali kan matsalolin Kasar – ACF

-

Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF) ta yi Allah-wadai da ’yan siyasa da ke fara yakin neman zabe na shekarar 2027, inda ta bukaci su mayar da hankali wajen magance matsalolin da ke addabar kasar nan maimakon fara yakin neman zabe a yanzu.

A yayin taron kwamitin zartaswa na kasa a Kaduna ranar Alhamis, shugaban ACF, Mamman Osuman, ya bayyana cewa ya kamata shugabannin kasar su maida hankali kan harkokin mulki da za su magance matsalolin da ‘yan Najeriya ke fuskanta, musamman a wannan lokaci, maimakon shigar da kai cikin harkokin siyasa.

Osuman ya kuma bayyana damuwarsa kan rashin rayuka a jihohin Filato, Edo, da Borno, da rikicin da ke gudana tsakanin Kogi da Enugu, musamman kan yankin Ette Community. Haka zalika, ya jaddada cewa matsalolin tattalin arziki da suka hada da tsadar rayuwa, kayayyaki, da sufuri suna daga cikin muhimman batutuwan da shugabanni ya kamata su mayar da hankali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara