DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar ‘yan sanda Kaduna ta yi nasarar ceto mutane 17 daga hannun masu garkuwa da mutane tare da kwato bindigu 21

-

 

 Jami’an sashin yaki da masu garkuwa da mutane na rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, tare da hadin gwiwar ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, sun ceto mutane 17 da aka yi garkuwa da su a ranar 3 ga Maris, 2025, daga Sarkin Pawa, jihar Neja.  

Rundunar ‘yan sandan ta bayyana cewa wannan nasara na daga cikin kokarin Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun, wanda ya jagoranci jami’an leken asiri da sauran hukumomin tsaro domin magance matsalolin tsaro. A cewar rundunar, an samu bindigogi kirar AK-47 guda 21 a sansanin masu garkuwar da aka kame.  

Daga cikin wadanda aka ceto sun hada da Williams Ubadia, Samuel Ezekiel, Ishaku Ishaya, Rebecca Ezekiel, da Victoria Ishaya, da sauran su. Dukkanin mutanen da aka ceto an kai su asibitin ‘yan sanda da ke Kaduna domin duba lafiyarsu, kuma an tabbatar da cewa suna cikin koshin lafiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara