DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jigo a jam’iyyar PDP Bode George ya ce shugaban riko na Rivers bai da hurumin naɗa muƙamai

-

Tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Olabode George, ya gargadi shugaban riko na jihar Ribas, Admiral Ibok-Ete Ibas mai ritaya, kan nade-naden da yake yi a kwanan nan da kuma sake fasalin hukumomin jihar.
Bode George ya bayyana hakan a matsayin abinda ya saba doka da kuma yiwuwar yin da na sani a gaba. 
Ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwar da aya fitar yau Jumu’a, inda ya bukaci Ibas da ya mutunta kundin tsarin mulki da bin doka da oda. 
Jigon na PDP ya kuma yi soka kan shugabannin rikon kwarya na kananan hukumomi 23 da ya naɗa, duk kuwa da umarnin da kotu ta bayar na haramta irin wadannan ayyuka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara