DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Atiku Abubakar: Ziyarar gaisuwar sallah muka kai wa Buhari, ba siyasa ba

-

Madugun adawar siyasar Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana cewa ziyarar da ya kai wa tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari a Kaduna ba ta da alaka da wata tattaunawa ko hadakar siyasa da ke da nasaba da zaben 2027.

Atiku, wanda ya jagoranci wasu fitattun ’yan siyasa ciki har da tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai da tsohon gwamnan Sokoto, Aminu Tambuwal, ya ce sun kai wa Buhari ziyara ne domin gaisuwar Sallah da sada zumunci. Ya kara da cewa, bayan ya kammala ayyukansa na Sallah a Adamawa, ya samu zarafin kai wa tsohon shugaban kasar ziyara.

Ziyarar na zuwa ne kwanaki biyu bayan gwamnonin jam’iyyar APC karkashin jagorancin Sanata Hope Uzodimma su ma suka kai irin wannan ziyarar gaisuwa ga Buhari. Wannan ya kara janyo ce-ce-ku-ce a fagen siyasa musamman kan makomar zabubbuka masu zuwa, amma Atiku ya jaddada cewa tafiyarsu ba siyasa ba ce.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara