DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda sun kama mahaifin da yake lalata da diyarsa budurwa mai shekaru 17 har ta samu ciki a Bauchi

-

 

Jami’an rundunar ‘yan sanda a Jihar Bauchi sun sanar da kame Umar Sule, mai shekaru 54, bisa zargin yin lalata da diyar cikinsa, budurwa mai kimanin shekaru 17 da haihuwa har ta samu ciki.

Kakakin hukumar, Ahmed Wakil, cikin sanarwar da ya fitar, ya ce sun samu korafi daga Abdullahi Baban Karatu, mai shekaru 55, daga kauyen Kurmin Ado, kan zargin da ake yi wa Sule na aikata laifin tare da diyarsa a lokuta daban-daban, wanda ya sabbaba ta dauki ciki na watanni uku, bisa ga rahoton likita.”

Sanarwar ta kara da cewa, kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Sani-Omolori Aliyu, ya umarci a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara