DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ku karbo Nijeriya daga hannun dattijan da ke shugabancin kasar – Femi Falana ya shawarci matasa

-

Fitaccen lauya mai rajin kare hakkin dan’adam, Femi Falana, SAN, ya shawarci matasan Nijeriya da su karbo kasar daga hannun dattijai ta dawo hannunsu.
Dan gwagwarmaya Falana ya bayar da wannan shawara ne a birnin Legas, yayin taron shekara-shekara karo na shida na jagorancin matasa, wanda aka lakaba wa suna ‘Resilience, Innovation, Social Responsibility and Entrepreneurship (RISE 2025).
Falana ya ce abubuwa ba su kasance kamar yadda suke a da ba, saboda haka ya zama wajibi matasa su kwato kasarsu kuma su sake fasalta ta yadda ya kamata.
Ya kara da cewa matasa suna shan wahala sakamakon halin da kasar ta shiga, saboda haka akwai bukatar matasa su tashi tsaye don zage damtse su yi abin da ya kamata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna kokarin bunkasa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan 1 – Kashim Shettima

Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya ce gwamnatin kasar na kan hanyar bunkasa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan 1 cikin shekaru goma masu zuwa. Kashim...

Yan sanda sun dakile yunkurin garkuwa da direba da fasinjoji a Katsina

Jami’an rundunar ‘yan sandan Nijeriya sun dakile wani yunkurin yin garkuwa da mutane a hanyar Funtua zuwa Gusau a Katsina. Jami’an sun yi artabu da ‘yan...

Mafi Shahara