DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sanata Ndume na shirin shiga hadakar Atiku – Daniel Bwala

-

Daniel Bwala, mai ba shugaban kasa Bola Tinubu shawara ta musamman kan harkokin siyasa, ya ce ya kamata jam’iyyar APC ta yi hattara da Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, yana mai zargin cewa lissafin dan majalisar da ruhinsa a siyasa sun bar jam’iyyar.

Bwala ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da ya yi da gidan talabijin na Channels, inda yake jan hankalin jam’iyyar APC musamman shugaban jam’iyyar, Abdullahi Ganduje, cewa Sanatan na a cikin jam’iyyar, amma ruhinsa na wani waje na daban.
Inda ya kara da cewa kamata ya yi Ndume ya fice daga jam’iyyar kai tsaye kamar yadda Nasiru El-Rufai ya yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara