DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Kano ta rufe wuraren kasuwanci 9 saboda ƙin biyan haraji

-

Jami’an hukumar tattara haraji ta jihar Kano sun rufe wuraren kasuwanci na wasu kamfanoni tara bisa zargin kin biyan kudaden haraji.
Daga cikin wuraren da aka rufe har da makarantu da wasu wuraren kasuwanci yayin zagayen rufe wuraren da tawagar KIRS ta gudanar.
A cewar jagoran tawagar jami’an hukumar Abbas Sa’idu, matakin da hukumar ta dauka ya zama dole domin kamfanonin sun kasa amsa wasikun da hukumar ta aika musu, tare da sanar da su kan bukatar biyan kudaden harajin da ake bin su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3

Wata kotu a Amurka ta yanke wa wani ɗan Najeriya mai zama a San Gabriel Valley, Abiola Femi Quadri, hukuncin ɗaurin shekara 11 da wata...

Natasha ta sake shan alwashin komawa majalisar dattawa a ranar Talata

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ‘yar Majalisar Dattawa daga jihar Kogi da aka dakatar, ta shigar da ƙara ga Majalisar Dattawa tana neman su girmama hukuncin Babbar...

Mafi Shahara