Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi watsi da ikirarin da ake na cewa tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a 2023, Rabi’u Musa Kwankwaso, na shirin komawa jam’iyyar APC.
Ya ce jam’iyyar NNPP ta bai wa ‘yan Nijeriya damar fahimtar abubuwan da jam’iyyar za ta iya yi ta hanyar ingantaccen shugabanci mai cike da gaskiya da rikon amana.
Idan dai za a iya tunawa a kwanakin baya ne shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dr,Abdullahi Umar Ganduje, ya yi hasashen komawar Kwankwaso jam’iyyar APC, inda ya jaddada cewa tsohon dan takarar shugaban kasa na shirin yin shiga.
Ganduje, wanda ya bayyana hakan a lokacin da ya karbi bakuncin kungiyar magoya bayan Tinubu, wadanda suka kai masa ziyara a Abuja, ya bayyana cewa jam’iyyar APC na ci gaba da karbar fitattun ‘yan siyasa ciki har da ‘yan majalisar tarayya.
Ya kara da cewa jam’iyyar na dakon dawowar Kwankwaso.